15 Janairu 2016 - 13:10
PDP ta bukaci a tube Shugaba Buhari

Jam’iyyar PDP a Najeriya ta bukaci Majalisar dokokin kasar da ta gaggauta tube shugaba Muhammadu Buhari daga mukaminsa sakamakon badakalar bacewar kundi mai kunshe da bayanai kan kasafin kudin kasar na wannan shekara da aka ce ya bata.

Sanarwar da mukaddashin kwamitn gudanarwa na PDP Uche Secondus, ya sanyawa hannu, ta kuma bukaci ministan kudin kasar Kemi Adeosun da na fasali Udo Udoma, da kuma gwamnan babban bankin kasar da su gaggauta yin marabus saboda rashin iya tsara siyasar tattalin arziki,lamarin da ya sa a yau ake sayar da takardar kudin kasar wato Naira 305 akan dalar Amurka daya.288